Shugaban Laberiya ya rage albashinsa da kashi 40

Shugaban Laberiya ya rage albashinsa da kashi 40%

Shugaban kasar Laberiya Joseph Boakai ya bayyana cewa zai rage albashin da yake karba da kashi 40 cikin dari.



A kwanakin baya ne dai al'ummar kasar Laberiya suka koka bisa tsadar rayuwa da 'yan kasar ke fama dashi wanda hakan yasa ake bincike kan albashin manyan ma'aikata dake kasar.


Kusan mutane biyar suna iya rayuwa a kasa da $2 (£1.70) a rana a cikin kasar dake yammacin Afirka.


Mista Boakai ya bayyana a watan Fabrairu cewa albashinsa na shekara yakai $13,400 ne,kuma zai rage shi zuwa $ 8,000.


Matakin na Boakai ya yi daidai da na magabacinsa, George Weah, wanda ya rage kashi 25 cikin 100 na albashinsa,wanda

wasu daga cikin al'ummar yammacin Afirka sun yaba da matakin na Mista Boakai, amma wasu na tunanin ko sadaukarwa ce da ganin cewa shi ma yana samun wasu abubuwa kamar alawus-alawus na yau da kullum.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp