Shugaba Tinubu ya soke ma'aikatu biyu

 

Shugaba Tinubu


A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar a larabar nan,ya ce ma'aikatun da abin ya shafa sun hada da ma'aikatar raya yankin Nije Delta da ma'aikatar wasanni.


Sanarwar ta ce yanzu za a hade ma'aikatun raya yankuna su dawo koma karkashin hukuma daya , kamar hukumar raya yankin Neja Delta, hukumar raya arewa maso yamma, hukumar raya kudu maso yamma, hukumar raya arewa maso gabas.


A cewar sanarwar majalisar zartaswa ta tarayya FEC ta kuma amince da hadewar ma’aikatar yawon bude ido da ma’aikatar al’adu da tattalin arziki.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp