Kwastam ta yi gwanjon litar man fetur 55,164 a Sokoto


Hukumar Kwastam mai kula da shiyyar Sokoto da Zamfara, a ranar Laraba, ta yi gwanjon litar man fetur 55,164 da ta kama daga hannun masu fasa-kwauri a Sakkwato.

Yayin da yake kaddamar da shirin Kwanturolan hukumar Kamal Muhammed, ya ce an gudanar da gwanjon ne bisa umarnin Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam, Bashir Adewale.

Ya kuma danganta matsalar karancin man fetur da ake fama dashi a fadin kasar nan da safarar shi da wasu suke, inda ya ce hukumar za ta dakile hakan domin inganta tattalin arzikin Najeriya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp