Gawar tsohon shugaban majalisar dattawa ta iso Nijeriya bayan shekaru uku da rasuwarsa.


Gawar tsohon shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Joseph Wayas, ta iso Nijeriya bayan kimanin shafe shekaru uku da rasuwarsa a turai.

Joseph Wayas, wanda ya kasance Shugaban Majalisar Dattawa tsakanin 1 ga Oktoba, 1979 zuwa 31 ga Disamba, 1983, ya rasu a wani asibiti a Landan a ranar 30 ga Nuwamba, 2021, yana da shekaru 80 bayan ya yi fama da rashin lafiya.

Matarsa ​​ta farko ta rasu bayan kwanaki 12, da rasuwarsa, an cigaba da ajiye gawar dan siyasar a dakin ajiye gawa har zuwa wannan lokaci.

1 Comments

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp