Ban tattauna batun sakin Nnamdi Kanu da gwamnonin Kudu maso Gabas ba – Obasanjo

 

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya ce bai tattauna batun sakin Nnamdi Kanu ba yayin ganawarsa da gwamnonin Kudu maso Gabas a jihar Enugu .

Daily Truth ta ruwaito a ranar Talata Obasanjo tare da Cif Emeka Anyaoku da Mai Martaba Igwe Alfred Nnaemeka Achebe, sun gana da gwamnonin Kudu maso Gabas.

Bayan kammala taron an yi ta rade-radin cewa taron ya tattauna batun sakin Nnamdi Kanu, wanda shi ne shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp