Babu wani abu tsakanin sarkin musulmi da gwamnan Sokoto:Fadar sarkin musulmi

Babu wani abu tsakanin sarkin musulmi da gwamnan Sokoto:Fadar sarkin musulmi

Babu wani abu tsakanin sarkin musulmi da gwamnan jihar sokoto Ahmad Aliyu,Dokta Muhammad Jabbi kilgori ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi a wajen bude taron jin ra’ayin jama’a kan gyaran dokar, Sa’in Kilgori, Dokta Muhammad Jabbi Kilgori, ya ce gyaran ba zai tube Sarkin Musulmi daga mulki ko ayyukansa ba.


Ya ce sabanin hasashe, babu wani batu tsakanin mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar da gwamna, Alhaji Ahmed Aliyu.


Kilgori, wanda ya zama hakimin Kilgori kuma dan majalisar masarautar, ya ce masarautar tana sane da wasu makiya da ke son haifar da matsala tsakanin masarautar da gwamnatin jihar.


Babu wani batu tsakanin Sarkin Musulmi da Gwamna Ahmed Aliyu ko kadan. Sarkin Musulmi a shirye yake ya yi aiki a karkashin kowace doka da aka zaba ta hanyar da ta dace. Mun yi aiki a ƙarƙashin dokoki daban-daban a baya kuma a shirye muke mu yi aiki a ƙarƙashin sabuwar doka.


Yace sarkin ya yi aiki a karkashin dokar da aka gabatar don gyara na tsawon shekaru 16. Sarkin Musulmi a shirye yake ya yi aiki kafada da kafada da gwamnati,


Aminiya ta ruwaito cewa gyaran da ake shirin yi a Sakkwato ta shekarar 2008 ya tayar da kura daga ciki da wajen jihar biyo bayan rade-radin da ake yi cewa gyaran ana shirin tsige sarkin musulmi ne

1 Comments

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp