Tinubu ya fi Obi da Atiku cewar wani jigi a jam'iyyar Labour Party.

Tinubu ya fi Obi da Atiku cewar wani jigi a jam'iyyar Labour Party.


Tsohon darakta janar na yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Doyin Okupe, ya bukaci ‘yan Nijeriya da kada su yi gaggawar hukunta gwamnatin shugaba Bola Tinubu.


A wata hira da aka yi da shi ranar a gidan talabijin na Channels, Okupe ya shawarci ‘yan kasar da su yi watsi da sukar gwamnatin Tinubu kamar gwamnatocin baya.


Ya ce shugaban kasar ya gaji matsalar tattalin arziki, inda ya kara da cewa ya hau kan karagar mulki ne a lokacin kasar tana cikin wani yanayi da ba a saba gani ba.


Don haka akwai bukatar a kara bashi dama domin a shawo kan matsalar tattalin arzikin kasar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp