Obasanjo ya shawarci gwamnoni su samar da Abinci don a samu saukin rayuwa

 Obasanjo ya shawarci gwamnoni su samar da Abinci don a samu saukin rayuwa





Tsohon shugaban Nijeriya Cif Olusegun Obasanjo ya shawarci gwamnonin jihohi da su mai da hankali kan samar da abinci tare da yin kira gare su da su ba da fifiko kan manufofin da suke inganta rayuwar mutane. 


Obasanjo ya ba bayyana hakan ne a ranar Laraba a Sokoto a wajen kaddamar da rukunin gidaje 136 da gwamnatin jihar Sokoto ta saya a kan kudi Naira biliyan 1.8. 


Tsohon shugaban kasar ya kasance a Sokoto a ziyarar kwanaki biyu don kaddamar da ayyukan da Gov. Ahmed Aliyu ya aiwatar yayin bikin cikarsa shekara daya kan mulkin jihar. 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp