Nnamdi Kanu na neman sulhu da gwamnatin Nijeriya


Jagoran masu fafutikar kafa kasar Biafra Nnamdi Kanu ya ce ai nemi zaman sasanci da sulhu tsakaninsa da gwamnatin Nijeriya bisa tuhumarsa da ake yi.

Kanu na magana ne ta hannun lauyansa Alloy Ejimakor, inda ya fada wa kotun tarayya a Abuja cewa zai nemi wannan sasanci ne karkashin doka ta 17 ta kotun tarayya.

Lauyan gwamnati, Adegboyega Awomolo ya ce tuni ya sanar da bangaren Kanu cewa ba ya da hurumin jagorantar wannan zaman sasanci a madadin gwamnatin tarayya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp