NLC da TUC sun janye yajin aiki a Nijeriya

 

NLC da TUC sun janye yajin aiki a Nijeriya 


Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC a Nijeriya sun sanar da janye yajin aikin da suka fara a ranar Litinin.


Shugaban kungiyar ta TUC Festus Osifo ya bayyana hakan ne a ranar Talata a Abuja bayan wani taron hadin gwiwa na majalisar zartarwa na kasa na hadin gwiwa na kungiyar.


Za a fitar da sanarwar nan ba da jimawa ba , in ji shugaban kwadagon.


A ranar Litinin ne kungiyoyin biyu suka tsunduma yajin aiki saboda korafe - korafensu kan karin kukldin wutar lantarki da kuma rashin cimma matsaya kan sabon mafi karancin albashi.


Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp