Gwamnantin tarayya ta bayyana ranar hutu domin tunawa da Dimokuradiyya.

Gwamnantin tarayya ta bayyana ranar hutu domin tunawa da Dimokuradiyya.

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba, 12 ga watan Yuni, 2024 a matsayin ranar hutu domin tunawa da ranar dimokradiyya ta bana.


Ministan harkokin cikin gida, Hon. Dr. Olubunmi Tunji-Ojo shi ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya a cikin wata sanarwa da babbar sakatariya a ma’aikatar Dr. Aishetu Gogo Ndayako ta fitar.


Ya ce, Yayin da muke bikin ranar dimokuradiyya a cikin tarihin kasarmu mai daraja, bari mu yi tunani a kan kokarin iyayenmu da suka kafa mu kuma tabbatar da cewa Nijeriya ta ci gaba da kasancewa kasa daya, amintacciyar kasa, zaman lafiya da rashin rabuwa.


Yayin da yake taya ‘yan Nijeriya murnar wannan rana, ya bukace su da su dage kan tsarin mulkin dimokradiyya.


Ministan ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kuduri aniyar kawo sauyi mai kyau domin farfado da tattalin arzikin kasa da inganta tsaro.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp