Gwamnan jihar Rivers Similaye Fubara ya umurci babban mai binciken kudi na jihar da ya gaggauta binciken asusun ajiyar kananan hukumomin jihar 23.
Umurnin Gwamnan na a binciki asusun ajiyar kananan hukumomin ya takaita ne a shekaru uku da suka gabata.
Wannan umurni dai na zuwa ne a lokacin da gabar siyasa ke kara zafafa tsakanin Gwamnan sa tsohon ubangidansa, ministan Abuja Nyeson Wike.
A lokacin da yake rantsar da sabbin kantomomin kananan hukumomin jihar, Fubara ya ce dalilin hakan shi ne don ya zama izna ga sabbin wadanda za su kama madafun iko.