Gwamna Rivers Fubara ya umurci a binciki asusun ajiyar kananan hukumomin jihar


Gwamnan jihar Rivers Similaye Fubara ya umurci babban mai binciken kudi na jihar da ya gaggauta binciken asusun ajiyar kananan hukumomin jihar 23.

Umurnin Gwamnan na a binciki asusun ajiyar kananan hukumomin ya takaita ne a shekaru uku da suka gabata.

Wannan umurni dai na zuwa ne a lokacin da gabar siyasa ke kara zafafa tsakanin Gwamnan sa tsohon ubangidansa, ministan Abuja Nyeson Wike.

A lokacin da yake rantsar da sabbin kantomomin kananan hukumomin jihar, Fubara ya ce dalilin hakan shi ne don ya zama izna ga sabbin wadanda za su kama madafun iko.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp