Alhazan kasar India sun koka da halin rashin kula a Saudiyya


Alhazan kasar India sun koka cewa ba a samar musu da abubuwan da suka kamata ba a aikin hajjin wannan shekarar na 2024.

Daga cikin abubuwan da suka rasa hada rashin tsafta a sansanonin Alhazai, karancin abinci, cunkoso musamman a Mina a lokacin gudanar da aikin hajjin bana.

Alhazan kasar ta India da suke cikin jerin kasashen Musulmin duniya da suka halarci wannan aikin hajji, sun zargi hukumar kula da aikin hajji na kasar da watsar da su.

Da yawa daga cikin alhazan dai sun saka a kafafen sadarwar zamani suna korafin yadda suka ce an ba a samar musu da wurare masu tsafta ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp