Shugaba Tinubu ya kaddamar da gangamin sanya yara kanana makarantun boko


Shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar da wani kamfen na inganta ilimi da bunkasar fasaha da daidaiton jinsi.


Gangamin da aka yi wa lakabi da, "duk daya muke" wato #WeAreEqual, wani shiri ne na kungiyar matan shugabannin kasashen Afirka OAFLAD.


An kaddamar da gangamin a kasashen Nahiyar Afirka 15 a fannoni daban-daban, inda aka mai da hankali kan kiwon lafiya, ilimi, karfafa tattalin arziki, da yaki da cin zarafin mata.


Da yake jawabi a wajen kaddamar da gangamin da aka gudanar a fadar shugaban kasa, Shugaba Tinubu ya jinjina wa kudurin matan shugabannin kasashen Afirka, a matsayinsu na mambobin kungiyar OAFLAD, na inganta daidaiton jinsi tare da takaita bambancin jinsi a fadin nahiyar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp