Majalisar dokokin jihar kano ta amince da dokar soke karin Masarautu guda 4 a jihar

Majalisar dokokin jihar kano ta amince da dokar soke karin Masarautu guda 4 a jihar.

Majalisar dokokin jihar Kano ta zartar da dokar majalisar masarautu ta Kano ta shekarar 2024 bayan kammala karatu na uku.

Dokar ta soke kafa sabbin masarautu guda 4 a jihar.

Dokar ta ce duk ofisoshin da aka kafa a karkashin dokar da aka soke, sabuwar dokar ta rushe su.

Haka zalika duk hakimai da aka karawa matsayi ko aka nada a karkashin dokar da aka soke za su koma kan mukamansu na baya.

Shugaban masu rinjaye kuma memba mai wakiltar mazabar Dala, Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa ne ya gabatar da kudirin gyaran sabuwar dokar a gaban zauren majalisar dokokin jihar Kano

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp