Kotu ta ki amincewa da bukatar Tukur Mamu


Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta yi watsi da bukatar Tukur Mamu, ta neman a dauke shi daga hannun Hukumar DSS zuwa gidan gyaran hali na Kuje.

A hukuncin da ya yanke, mai shari’a Inyang Ekwo, ya yi watsi da bukatar Mamu saboda rashin tsaro a gidan yarin.

Mai shari’a Ekwo, ya jaddada umarnin da ya bayar tun farko cewa a bar Tukur Mamu ya samu damar zuwa wurin likitansa domin jinya bisa kulawar jami’an lafiyan DSS.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp