Gwamnatin tarayya ta musanta zargin karkatar da kudin 'yan fansho zuwa wani fanni.

Gwamnatin tarayya ta musanta zargin karkatar da kudin 'yan fansho zuwa wani fanni.

Gwamnatin tarayya ta musanta zargin da ake cewa tana shirin karbar bashin N20tn na fansho domin bunkasa ababen more rayuwa.




Ministan kudi kuma mai kula da harkokin tattalin arzikin Nijeriya Wale Edun, ya ce gwamnati za ta bi ka’idojin da aka kafa na asusun fansho domin yin abinda ya dace.




An ruwaito cewa ministan ya shaidawa manema labarai bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya na kwanaki biyu a fadar shugaban kasa a ranar Talata cewa, gwamnati za ta bayyana shirin yin amfani da kudaden kananan hukumomi da suka hada da asusun don samar da ababen more rayuwa.




Sai dai a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Alhamis, Edun ya bayyana cewa,harkar fensho, tana da kayyadaddun tsarin doka ta musamman wajen tafiyar da ita.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp