Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar tantance lafiya kafin aure


Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya rattaba hannu kan dokar tantance lafiyar masu son yin aure.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce dokar na nufin daga yanzu babu wani aure da za a ɗaura shi a Kano ba tare da gabatar da sakamakon gwajin lafiya ba.

Hakan na nufin rage yiwuwar haihuwar yara masu wasu matsalolin kiwon lafiya kamar sikila, cutar kanjamau da ciwon hanta.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp