Yanzu-yanzu:
Jirgin kamfanin Dana ya yi hatsari a filin jirgin sama na Lagos
Wani jirgin saman kamfanin Dana Air ya yi hatsari a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke birnin Lagos da safiyar Talatar nan.
Rahotanni sun bayyana cewa ba a samu asarar rai ba kamar yadda Jaridar Leadership ta rawaito.
Har zuwa wannan lokacin ba a samu cikakkun bayanai da game da afkuwar lamarin ba.