Lamarin kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, ya faru ne a daren Asabar.
Maharan da suka yi kukan-kura suka afka a rumbun, sun kuma fasa wasu shagunan 'yan kasuwa, suka saci kayan abinci can ma.
Kazalika, sun kuma tare wata tirela makare da kayan abinci da aka ba gwamnatin jihar Kebbi ta kayan abinci, nan ma suka wawashi hatsi.
Da ya ke ganawa da manema labarai, Muhammad Gwadangwaji, wanda shi ne shugaban 'yan kasuwar na Bayan Kara Birnin Kebbi, ya ce matasan sun kuma banka wuta ga wasu rumbunan adana kaya 'yan kasuwa.