Mutane da yawa sun makale yayin da gini ya ruguje a Kano.
Yanzu haka dai wasu ma’aikata da ba a tantance adadinsu ba sun makale a wani gini da ya rufta a unguwar Kuntau da ke karamar hukumar Gwale a jihar Kano.
Wata majiya ta bayyana cewa, akalla mutane 11 ne suka makale a karkashin baraguzan ginin.
Jami’an hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) sun garzaya da wasu mutane biyu da aka ceto zuwa asibiti.
A halin yanzu ana ci gaba da tono wasu gawarwaki da
Har yanzu ba a tantance adadin su ba.