Babban layin wutar lantarki na Nijeriya ya sake faduwa.

 Babban layin wutar lantarki na Nijeriya ya sake faduwa.




Kamfanin samar da wutar lantarki guda daya ne kawai ke aiki kamar yadda bayanai daga cibiyar mai zaman kanta (ISO) reshen kamfanin watsa labarai na Nijeriya ya bayyana.


Wannan shine karo na shida da Babban layin wutar yana faduwa a shekarar 2024 da muke ciki.


Daily Trust ta rawaito cewa da misalin karfe 8 na safiyar ranar Litinin, sabbin bayanai da hukumar ta ISO ta fitar sun nuna cewa a halin yanzu tashar tana samar da wutar lantarki mai karfin mega watt266.50.


Da yake tabbatar da faduwar layin wutar a cikin wata sanarwa, Jos Disco ya ce Katsewar da ake fuskanta a halin yanzu a cikin jihohinmu ya samo asali ne daga cibiyar sadarwa ta kasa. Kuma faduwar layin wutar ya afku ne da sanyin safiya da misalin karfe 02:42 na yau litinin 15 ga watan Afrilu 2024, wanda hakan ya sa aka samu katsewar wutar lantarki ga dukkan bangarorin Nijeriya.


Shugaban Kamfanonin, Dakta Friday Adakole Elijah, ya bayyana fatan cewa za a dawo da grid din don samar da wutar lantarki ga masu amfani da ita da kuma kwastomin su.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp