Tinubu ya umurci a kubutar da daliban jihar Kaduna

 

Tinubu ya umurci a kubutar da daliban jihar Kaduna

Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah-wadai da sace ‘yan gudun hijira a Borno da kuma dalibai a jihar Kaduna.

Ajuri Ngelale, mashawarcin shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma


’a a Abuja.

Ngalale ya ce shugaban kasar ya umarci jami’an tsaro da na leken asiri da su gaggauta ceto wadanda lamarin ya shafa tare da tabbatar yin hukunci a kan wadanda suka aikata wannan aika-aika.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp