Remi Tinubu ta bukaci a yi dokar hukuncin kisa ga masu garkuwa


Remi Tinubu ta bukaci a yi dokar hukuncin kisa ga masu garkuwa

Uwargidan shugaban kasa, Sen. Oluremi Tinubu, ta yi kira da a samar da dokokin da za su aiwatar da hukuncin kisa ga duk wanda aka samu da laifin satar mutane a kasar nan.

Uwargidan shugaban kasar ta bayyana haka ne a ranar Juma’a yayin wata ganawa da ta yi da shugabar matan jam’iyyar APC ta kasa a fadar shugaban kasa.

Ta koka da irin yadda masu garkuwa da mutane ke girbi daga ‘yan Najeriya suna kashe su, inda ta ba da misali da halin da ake ciki a yanzu da aka yi garkuwa da mutane akalla 200 a Kaduna da sauran wadanda aka kashe daga jihar Borno.


Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp