Sheikh Ibrahim Khalil ya bukaci gwamnan Kano ya bada murja kunya a matsayin mataimakiya ta musamman.

 Shahararren Malamin Addinin Musulunci ya bukaci Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya nada, Murja Kunya a matsayin mai Taimakawa gwamnan ta musamman a Social Media.


Sanannen malamin addinin musulunci, Sheihk Ibrahim Khaleel, ya bukaci gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, da ya nada , Murja Ibrahim Kunya yar Tik Tok,a matsayin babbar mataimakiya ta musamman kan kafafen sadarwa na zamani.


Sheikh Khalil ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadin da ta gabata a cikin wani shiri da yagabatar a tashar Freedom Radio da ke Kano.



Malamin yace yin hakan zaitamakawa gwamnati da al'umma kwarai da gaske wajen,tallafawa mata musamman yan social media ta yadda za'a fito da sabbin hanyoyin kasuwanci na zamani da zai taimaka ta shafukan sada zumunta.



A kwanakin baya ne Hukumar hisbah ta jihar kano ta gurfanar da murja Ibrahima a gaban wata kotun shari’ar Musulunci  karkashin jagorancin Nura Yusuf Ahmad ta bayar da umarnin cewa, Murja Ibrahim Kunya a kaita asibiti domin ayimata gwajin tabin hankali a wani asibitin gwamnati domin sanin halin da take ciki.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp