NiMet ta yi hasashen za a yi rana a wasu jihohin Nijeriya


 NiMet ta yi hasashen za a yi rana a wasu jihohin Nijeriya



 Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya, NiMet, ta yi hasashen hasken rana da jin dadi daga ranar Litinin zuwa Laraba a fadin kasar.


 An fitar da hasashen yanayi na NiMet ranar Lahadi a Abuja, inda aka yi hasashen yanayi za a iya samun yanayi na rana daga ranar Litinin a yankin arewa.


A cewarta, ana sa ran samun gizagizai tare da hasken rana a jihohin Arewa ta Tsakiya da ake sa ran za a iya samu yanayin tsawa a sassan jihar Benue da safiyar Laraba.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp