Muna ba da shawara ga Gwamnatin Kano da ta nemi afuwar Daurawa - Abdallah Gadon Kaya 

 Muna ba da shawara ga Gwamnatin Kano da nemi afuwar Daurawa - Abdallah Gadon Kaya 



Fitaccen malamin addinin Musulunci daga jihar Kano Dr. Abdallah Usman Gadon Kaya ya yi kira tare da bayar da shawara ga gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf da ya nemi afuwar Sheikh Aminu Daurawa.


Dakta Gadon Kaya ya yi kiran ne a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta na facebook a ranar Juma’a jim kadan bayan Sheikh Daurawa ya ayyana yin murabus daga shugabancin hukumar Hisbah.


 

Ya ce "Muna kira ga gwamna Abba Yusuf tare da makusantansa da su kai zuciya nesa su kira malam Daurawa, su zauna da shi kuma su ba shi haƙuri kan abubuwan da ya faru."

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp