MTN ya kulle layukan waya 4.2m da aka kasa hada su da lambar NIN


 MTN ya kulle layuka 4.2m da aka kasa hada su da lambar NIN


Kamfanin sadarwa na MTN a Nijeriya ya ce ya katse layukan sadarwa akalla miliyan 4.2 daga cibiyar sadarwarsa yayin da wa'adin da aka kayyade na ranar 28 ga watan Fabrairu na a hada lambobin layuka da shaidar zama dan kasa (NIN) da SIM ya cika.



Kamfanin MTN ya bayyana hakan ne a sakamakon binciken da ya gudanar a ranar Juma’a.

Kamfanin ya ce layukan da aka katse sune na mutanen da suka yi kunnen kashi suka ki hada shi da lambar shaidar zama dan kasa wato NIN.  


A cewar kamfanin, tun a cikin watan Disambar  2023 ne hukumar NCC ta ba da umurni ga dukkanin kamfanonin sadarwa a  kasar da su tabbatar masu masu amfani da layukan sadarwa su hada layukan wayoyinsu da NIN ɗin su.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp