Shan miyagun kwayoyi ke sa karuwar rashin tsaro a Nijeriya - Marwa

 

Shan miyagun kwayoyi ke sa karuwar rashin tsaro a Nijeriya - Marwa

Shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya NDLEA, Buba Marwa, ya ce shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin ‘yan kasar ne ke haddasa rashin tsaro a kasar.

Marwa ya bayyana haka ne a yayin taron wayar da kan mata da matasa a babban birnin tarayya Abuja ranar Juma’a a Abuja.

Ya kuma ce matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa ita ce matsalar kowa wanda a cewarsa ya hada da iyaye da makaranta da sauran jama’a da su kansu matasa.


Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp