Kwastam sun mika wasu motoci 6 makare da abinci ga masu kayan

 

Kwastam sun mika wasu motoci 6 makare da abinci ga masu kayan


Hukumar Kwastam ta Jihar Katsina ta hannanta wasu manyan motoci guda shida makare da kayan abinci ga masu su kamar yadda Shugaba Bola Tinubu ya ba su umurni.

Motocin da aka mika su ga masu su an tare su ne a shingen binciken kan iyakar Kongolam da ke karamar hukumar Mai-Adua a jihar Katsina.

Shugaban ya bayar da umurnin ne da nufin tabbatar da an samu wadatar abinci da kuma rage wahalhalun da akasarin ‘yan kasar ke fuskanta.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp