Hukumar Kwastam a Najeriya reshen jihar Kano, ta ce ta samu kudaden shiga har Naira biliyan 9.7 a watan Fabrairu.

Hukumar hana fasa kwauri ta Nijeriya kwastam  NCS, reshen jihar Kano, ta samu karin kudin shiga Naira biliyan 9.7 a watan Fabrairu a daga mutanen da suke shiga da kayayyakin kasashen waje zuwa kasar.

Dauda Chana, shine kwanturolan Hukumar Kwastam mai kula da jihohin Kano da Jigawa ya bayyana hakan a wata tattaunawa da ya yi da Kamfanin Dillancin labaran Nijeriya (NAN)a Kano .


 Chana ya kuma ce rundunar ta samar da matakan hana fitar kudaden shiga ta matsugunan kan iyakokin yankin ta hanyar karfafa tsaro da sa ido domin dakile safarar haramtattun kayayyaki a kasar.


Ya kara da cewa rundunar za ta ci gaba da gudanar da gwajin kashi 100 na kayan da ke shiga ta kan iyakokinta domin hana shiga da kayayyaki da suka hada da makamai da alburusai.


Kwanturolan ya bayyana cewa,rundunar ta bayar da umarnin gudanar da aiki mai inganci ga jami’anta da ke kan iyakokin kasar kan yadda za a shawo kan matsalar fasa kwauri,kuma zasu cigaba da inganta harkokin kasuwanci a fadin kasar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp