![]() |
Malam Aminu Ibrahim Daurawa |
Hukumar Hisbah a jihar Kano sun kama wasu mutane 10 da ake zargi da aikata baɗala a wani gidan Gala da ke a jihar
Samamen ya biyo bayan ƙorafi da mabiya addinin kirista dake titin Zungeru a karamar hukumar Fagge suka kai ga hukumar.
Mazauna yankin sun koka da cewa an bude gidan Gala dinne a cikin unguwar su, don haka ne suka shigar da kara ta hannun lauyoyinsu.