Hisbah ta kai samame Gidan Gala a Kano

Malam Aminu Ibrahim Daurawa 

Hukumar Hisbah a jihar Kano sun kama wasu mutane 10 da ake zargi da aikata baɗala a wani gidan Gala da ke a jihar 

Samamen ya biyo bayan ƙorafi da mabiya addinin kirista dake titin Zungeru a karamar hukumar Fagge suka kai ga hukumar.

Mazauna yankin sun koka da cewa an bude gidan Gala dinne a cikin unguwar su, don haka ne suka shigar da kara ta hannun lauyoyinsu.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp