Tsohon gwamnan jihar Bauchi, Isa Yuguda, ya bayyana cewa har yanzu gwamnatin tarayya na biyan tallafin man fetur.
Tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne a wata hira a gidan Talabijin na Channels a ranar Litinin data gabata.
A ranar 29 ga Mayu, 2023, Tinubu ya ayyana kawo karshen tallafin man fetur a lokacin jawabinsa na farko.
Asusun ba da lamuni na duniya IMF cikin wani rahoto da ya bayar a watan da ya gabata ya kuma shawarci Najeriya da ta daina kashe kudaden tallafin mai da wutar lantarki gaba daya a wani mataki na magance kalubalen tattalin arzikinta.