Har yanzu Najeriya na biyan tallafin man fetur - Isa Yuguda


Tsohon gwamnan jihar Bauchi, Isa Yuguda, ya bayyana cewa har yanzu gwamnatin tarayya na biyan tallafin man fetur.

Tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne a wata hira a gidan Talabijin na Channels a ranar Litinin data gabata.

A ranar 29 ga Mayu, 2023, Tinubu ya ayyana kawo karshen tallafin man fetur a lokacin jawabinsa na farko.

Asusun ba da lamuni na duniya IMF cikin wani rahoto da ya bayar a watan da ya gabata ya kuma shawarci Najeriya da ta daina kashe kudaden tallafin mai da wutar lantarki gaba daya a wani mataki na magance kalubalen tattalin arzikinta.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp