Gwamnatin Kebbi ta rage sa’o’in aiki ga ma’aikatan gwamnatin jihar


Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya rage lokutan aiki ga ma’aikatan gwamnatin jihar a cikin wannan watan na Ramadan.

Kwamishinan ma’aikatar fansho da horaswa na jihar Auwal Manu-Dogondaji ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Birnin Kebbi a yau Talata.

Ya ce matakin zai baiwa ma’aikatan gwamnati damar gudanar da ibada cikin sauki.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp