'Yan majalisar Najeriya na fatan mayar da shugabancin kasar tsarin Prime minister


 

‘Yan majalisar dokokin Najeriya 60 sun kada kuri’a kan bukatar sauya tsarin tafiyar da gwamnatin Najeriya zuwa tsarin gwamnatin Prime minister a maimakon shugaban kasa wanda aka fara amfani da shi a jamhuriya ta farko.

‘Yan mahalisar su 60 sun gabatrwa majalisar wani kwarya-kwaryan kundin tsarin mulki, wanda suke ganin matukar aka bi shi, za’a yi nasarar mayar da kasar kan tsarin na Prime minister nan da shekara ta 2031.

 

Da yake yiwa manema labaran fadar shugaban kasa jawabi bayan gabatar da kundin, mai magana da yawun yan majalisar su 60 Abdulsamad Dasuki, ya ce lokaci yayi da ya kamata a kawo karshen tsarin shugaban kasa mai cikakken iko a Najeriya, la’akari da tsadar da yake da shi.

Duk da dai ‘yan majalisar sun nuna shakku game da samun nasarar sauya tsarin gwamnatin kasar nan da shekara ta 2031, amma sun ce karfin da tsarin shugaban kasa mai cikakken iko ya baiwa shugaban kasar ya yi yawan da yake janyo ci baya ga kasa.

 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp