Tinubu na ganawa da tawagar kungiyar kwallon kafar Nijeriya Super Eagles


 Tinubu na ganawa da tawagar kungiyar kwallon kafar Nijeriya Super Eagles

Shugaba Tinubu yana ganawa da kungiyar Super Eagles a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Kungiyar Super Eagles dai ta sha kashi da ci 2-1 a hannun mai masaukin baki Ivory Coast a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Afirka na shekarar 2023 a ranar Lahadin data gabata.

Bayan kammala wasan, shugaba Tinubu ya jinjina wa Super Eagles bisa jajircewar da suka nuna a wasan karshen.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp