Jam'iyyar APC ta yi gargadi kan rusa masarautun Kano

 Jam'iyyar APC ta yi gargadi kan rusa masarautun Kano. 




Jam’iyyar adawa ta APC ta gargadi gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da ya yi taka-tsan-tsan don gudun kada a tura shi yin wani abu da zai iya shafar zaman lafiya da ake samu a jihar Kano. 


 Jam’iyyar APC ta yi gargadin cewa duk wani yunkuri na kawo cikas ga tsarin masarautun, kamar yadda Ganduje ya kirkiro, na iya tayar da zaune tsaye a garin muddin suka dauki matakin hakan kamar yadda jaridar Punch ta rawaito.


A ranar 5 ga watan Fabrairu ne wata kungiya mai suna‘Yan Dangwalen Jihar Kano ta rubutawa Majalisar Dokokin Jihar Kano, takardar neman a sake duba dokar kafa karin masarautu hudu a Gaya, Rano, Karaye, da Bichi da gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje ta yi.


Kungiyar ta kuma yi kira da a mayar da tsohon Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp