EFCC ta kwato sama da naira biliyan 60 cikin kasa da kwanaki 100


 

Hukumar hana cin hanci da rashawa ta EFCC ta sanar da kwato naira biliyan 60 cikin kasa da kwanaki dari, yayin da ta karbi korafe-korafen cin hanci guda dubu 5.

Yayin da yake jawabin ayyukan da yayi cikin kwanaki 100 da zaman sa shugaban hukumar Mr Ola Olukoyede ya ce cikin korafe-korafe dubu 5 din da aka shigar gaban hukumar ta amince a fara bincike kan sama da dubu 3.

Ya ce bayan naira biliyan 60 din an kuma kwato wata dala miliyan 10 cikin kasa a watanni 4 da yayi a ofis.

Mr Ola ya ce lamarin cin hanci da rashawa abu ne da ke bukatar hadin kan jama’ar kasar kasancewar EFCC ba zata  iya ita kadai.

Baya ga wannan jamawabi, shugaban na EFCC yayi korafi game da karancin ma’aikata, yana mai cewa hukumar da ke sanya idanu kan mutane sama da miliyan 150, tana da ma’aikata 4,800 don haka ba za’a ga tasirin aikin da suke yi ba.

 

 

1 Comments

  1. To ai a banza don an kwace a hanun wani, don nasan kuma zasu koma a aljihun wani, don haka ina kira da EFCC da su kawo kudin na aje su a wajena

    ReplyDelete
Previous Post Next Post