Gwamnatin tarayya ta sake gargadin NLC game da shirin zanga-zanga


 

Gwamnatin tarayya ta sake gargadin kungiyoyin kwadago a Najeriya kan shirin zanga-zanga da suke yi a cikin makon nan.

Wannan na zuwa ne bayan da wasu kungiyin fararen hula 65 suka nuna goyon bayan su ga kungiyoyin kwadagon da kuma tabbatar musu da bada goyon baya a ranar zanga-zangar.

A karshen makon jiya ne shugaban kungiyar NLC Joe Ajero ya zargi gwamnatin tarayya da shirya ‘yan dabar da zasu kai musu hari a ranar zanga-zangar, zargin da gwamnati ta musanta.

Da yake jawabi babban mai taimakawa shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Mr Bayo Onanuga ya ce tuni ‘yan sanda suka mikawa kungiyoyin daya bayan daya takardun gargadin fita zanga-zangar don haka abu mafi a’ala shine su janye kudurin nasu.

Sai dai kuma duk da wannan gargadi da gwamnatin tarayya ta sabunta, kungiyar ta NLC ta ce babu gudu ba ja da baya wajen gudanar da zanga-zangar gobe Talata da kuma jjibi Laraba.

Post a Comment

Previous Post Next Post