Wike zai haramta zirga-zirgar motocin haya marasa alamar Tãzi a Abuja


Ministan babban birnin tarayya Najeriya Nyesom Wike, ya ce nan ba da dadewa ba, hukumar gudanarwar babban birnin tarayyar za ta haramtawa motocin haya marasa fenti da ke nuna alamar tãzi yin aiki a kan titunan birnin ƙasar.

Ministan ya fadi hakan yayin da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, ya bayyana cewa shirin na da nufin magance matsalar tsaro da ta addabi yankin. 

Jaridar Leadership ta ruwaito Wike yana jaddada bukatar daukar tsauraran matakai don kawar da duk wasu bata gari a ciki da wajen  birnin tarayya Abuja.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp