Jihohin katsina da Jigawa sune a kangaba wajen mutuwar mutane Dalilin Hatsari inji FRSC.

 Jihohin Katsina da Jigawa ne a sahun gaba wajen yawan mutuwar mutane ta dalilin hatsari a 2023 - FRSC


Hukumar Kiyaye aukuwar haddura ta kasa FRSC ta bayyana cewa a cikin Shekarar 2023,anfi Samun hatsari a hanyoyin, Jigawa, Katsina, Kwara da jihar Osun. 


Jami’in hukumar FRSC Dauda Ali Biu, ya bayyana hakan a wata zantawa da manema labarai  yayi a yau litinin, Inda yace saboda Manyan motoci, dake tafiye tafiye a hanyoyin tareda motocin daukar kaya da rashin kyan hanya ya haifar da Lamarin. 


Yace sashin ‘Operation Zero Tolerance’ wani aiki ne na sintiri na musamman da rundunar ta fara a watan Disambar 2023 domin dakile hadurran ababen hawa a Kasar nan.


Tsakanin 15 ga Disamba, 2022, da 15 ga Janairu, 2024, kwamitin binciken ya gudanar da ayyuka na musamman, jimillar hadurran titunan da aka samu yakai 634 kuma  sun faru a duk fadin najeriya, sabanin 535 a wannan lokacin a shekarar 2022, wanda ya nuna karuwar kashi 19 cikin dari na hadduran dake faruwa a najeriya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp