Tinubu na rokon Super Eagles da su doke Kamaru a gasar AFCON.

 Tinubu na rokon Super Eagles da su doke Kamaru a gasar AFCON


Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya roki ‘yan wasan Super Eagles da su yi duk mai yiwuwa don ganin sun samu nasara a yayin da Najeriya zasu fafata da babbar abokiyar hamayyarta, Kamaru a gobe, domin buga wasan dab da na kusa da na karshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake yi a Cote d’Ivoire. .


An isar da sakon shugaban kasar ga tawagar ta hannun ministan raya wasanni, Sanata John Owan Enoh, inda ya bukaci Super Eagles da su jajirce wajen tunkarar abokan karawarsu a wasan zagaye na 16 mai mahimmanci na gobe asabar.


Kamar yadda wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimakiya ta musamman ga sanata Enoh, Diana-Mary Tiku Nsan, ta bayyana cewa ‘yan Super Eagles sun sanar da cewa shugaban kasar na bin kungiyar ne domin yayi duk abinda ya dace a kansu, don haka dole ne su rubanya kokarinsu domin ‘yan Nijeriya da suke gida su samu Farin ciki da wannan wasa .

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp