Shugaba Bola Tinubu ya rattaba hannu kan kasafin kudin bana

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan kasafin kudin bana jim kadan bayan komawar sa Abuja daga jihar Lagos inda ya gudanar da hutun kirismeti.


Ko da yake jawabi jim kadan bayan rattaba hannu kan kasafin kudin, shugaba Tinubu ya tabbatarwa da ‘yan Najeriya cewa ba za’a ja kafa ba wajen fara aikwatar da kasafin kudin.

Ya kuma baiwa dukannin ma’aikatu da hukumomin gwamnati umarnin fara shirin amfani da kasafin kudin na bana ba tare da bata lokaci ba.

Manyan bangarorin da ke gaba a kasafin kudin na bana sun hadar da Tsaro, samar da ayyukan yi, inganta tattalin arziki, alkinta muhalli, gina dan adam, da kuma yaki da talauci.

Kasafin kudin na bana ya kama Naira Triliyan 28.7

 

 


 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp