Sarkin Musulmi ya ce a sa ido dan dubar jinjirin watan Rajab


Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya, Alhaji Sa’ad Abubakar na uku, ya umurci al’ummar Musulmi su fara duba jinjirin watan Rajab daga Juma’a 12 ga watan Janairu.

Sanarwar duba watan na Rajab ta fito ne daga shugaban Kwamitin Ba da Shawarwari kan Al’amuran Addinin Musulunci, Farfesa Sambo Janaidu.

Yace, idan aka samu labarin jinjirin Watan sai a mika rahoton hakan ga Hakimi ko mai unguwa mafi kusa don sadarwa ga Sarki.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp