Hukumar Kwastam ta samu Karin kudaden shiga na Tiriliyon N3.206


Hukumar Kwastam a Najeriya ta ce ta tattara kudaden shiga na Naira Tiriliyan 3.206 a shekarar data gabata ta 2023, wanda hakan ya nuna cewa an samu karuwar kashi 21.4 a cikin dari daga Naira tiriliyan 2.64 da aka samu a shekarar 2022.

Babban Kwanturolan Hukumar Kwastam, Mista Adewale Adeniyi, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai, a Abuja jiya Laraba.

Adewale Adeniyi yace hukumar ta samu gagarumin ci gaba ta hanyar tattara kudaden shiga na Naira tiriliyan 3.206, a shekarar 2023, wanda hakan ya nuna cewa an samu karin kashi 21.4% daga jimillar kudaden shiga na shekarar da ta gabata na Naira tiriliyan 2.641.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp