Nijar ta karfafa hulda tsakaninta da Iran

Kasar Jamhuriyar musulinci ta Iran ta yi alkawalin karfafa tallafin da take ba wa jamhuriyar Nijar

Mahukunta birnin Teheran din sun bayyana hakan ne a yayin ziyarar Firaministan Nijar Ali Mahaman Lamine Zeine ya kai a kasar ta Iran bayan a makon da ya gabata ya kai irin ta a Rasha

Mataimakin shugaban kasar Iran din Muhammad Mukhber ya bayyana wa tawagar ta Nijar hakan inda ya ce kasar tasa za ta karfafa taimaka wa Nijar domin rage mata radadin takunkumin ECOWAS da aka kakabawa kasar tun bayan juyin mulki

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp