Mutane dubu 30 zamu dauka cikin dubu 400 da suka nemi aikin dan sanda- Hukumar kula da 'yan sanda

Hukumar kula da ayyukan ‘yan sanda ta kasa ta ce mutane dubu 30 kachal zata dauka aiki, cikin sama da dubu 400 da suka nemi aikin a bana.

Ta cikin wata sanarwa da shugaban hukumar Solomon Arase ya fitar ta ce sama da mutane dubu 400 ne suka nemi aikin dan sanda cikin makonni 6 kachal da bayar da sanarwar.

Hukumar ta ce zata fara tantance wadanda suka nemi aikin don tsamo wadanda suka chanchanta a gobe litinin 8 ga watan da muke ciki na Janairu.

Arase wanda tsohon Supeton ‘yan sanda ne ya ce ma’aikatan hukumar zasu zabi ma’aikata ne bisa chanchanta, don haka ya gargadi masu yunkurin amfani da sanayya wajen samun aikin da su kuka da kansu matukar aka kama su.


 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp