Matashi ya hallaka abokin aikinsa a Ja’en da ke Kano





Wani matashi ma’aikacin wani kamfani a Kano ya halaka abokin aikinsa a unguwar Ja’en. 

Kawo yanzu ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro sun jefa borkonon tsohuwa domin kwantar da hankali bayan wata hatsaniya da ta biyo bayan lamarin. 

Mai magana da yawun ‘yan sandan Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce sun tura jami’ansu don dawo da doka da oda, amma ya ce kawo yanzu suna kan tattara bayanan dalilin kisan da ma sauran abubuwan da suka faru a kan lamarin.




Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp