Bakin talaucin da ya addabi Nijeriya ya ragu da kaso 7%, inji Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi kiyasin cewa bakin talaucin da ake fama da shi a kasashen Nijeriya da Tanzania ya ragu da kaso 7% a cikin shekaru uku da suka gabata.

A cikin wani babban kundi da bankin duniyar ya fitar, ya sanar cewa a cikin shekaru ukun, an kuma samu karuwar samun aikin yi da kaso 8% a bangarorin gwamnati da masu zaman kansu.

A cikin kundin, babban mai bibiyar tattalin arzikin Nahiyar Afrika na bankin duniya, Mr Andrew Dabalen, ya sanar cewa hakan ta faru ne ta dalilin amfani da kafafen sadarwar zamani da wayoyin hannu na salula.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp