Mahaifiyar Gwamna Abba na addu'ar a mayar da Sanusi mukamin Sarkin Kano


A cikin wani fai fan bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta an hango mahaifiyar gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, Hajiya Naja’atu Yusuf, na addu’o’in neman a mayar da tsohon Sarkin Kano, Muhammad Sanusi na biyu akan karagar mulki. 

Indai za ku iya tunawa gwamnatin data shuɗe ta gwamna Abdullahi Umar Ganduje ta sauke sa.

Mahaifiyar Gwamnan ta yi addu’ar Allah ya mayar da tsohon sarkin kan karagar sarakunan ‘Gidan Dabo’ domin ya ci gaba da gudanar da ayyukan da ya fara kafin a sauke shi.

Bidiyon wanda aka wallafa a ranar juma’a, wani bangarene na ziyarar taya murna biyo bayan hukuncin da kotun koli ta yanke wanda ta tabbatar da zaben Abba Gida-Gida.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp